Wannan wani Ango ne da ya daga amaryarsa sama a tsakiyar mutane.
A cikin Bidiyon nasa da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta, an ji ana ta guda.
Wasu sun ce bai kamata ba inda wasu ke cewa ai matarsa ce.
https://www.tiktok.com/@aminuabdulrazaq359/video/7630618801142238485?_r=1&_t=ZS-95hXUlqBFa5
Ummu faizan ta bayar da labarin cewa, tsohon mijinta yace zai kara aure inda ita kuma ta nemi ya saketa.
Tace ba wai dan kishi ba, sai dan baya iya gamsar da ita rayuwar aure.
Tace wani lokacin a sati sau daya kawai suke yi.
Tace duk da haka ta hakura ta dauka kaddararta kenan, kuma lura da cewa, sun haihu.
Tace kwatsam sai yace zai kara aure, tace sai take ganin itama ya kasa gamsar da ita, ya zai iya gamsar da mata 2.
Tace dalili kenan yasa ta nemi ya saketa, tace da ya kaita kara gurin iyayenta da abokai, amma da mahaifinta ya ji dalili sai ya goyi bayanta.
Tace ta samu ta sake aure kuma sabon mijin data aura yana gamsar da ita gashi har ta dauki ciki.
Tace matar da tsohon Mijinta ya aura itama ta rabu dashi.
Tace sai gashi yana kiranta wai ta kashe auren da ta y...
An bayyana wadda ta lashe gasar Sarauniyar Kyau ta Kano a shekarar 2026.
An ganta sanye da wata farar Riga tana rawa.
https://www.tiktok.com/@faceofhopeofficial/video/7630589199435189525?_r=1&_t=ZS-95hULwxPgUy
Malamin Addinin Islama, Bangaren Darika, Dr. Junaid ya bayyana cewa, Rawa ba Haramun bace.
Malam yace ba laifi bane idan waka ta maka dadi ka dan tashi ka yi rawa.
https://www.tiktok.com/@hidayah_ta_annabi/video/7629473030606966036?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7629473030606966036&source=h5_m×tamp=1776700582&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=271a3835-677e-4613-94ea-137f7bc45859&share_app_id=1233&ugbiz_name=MAIN&ug_btm=b2...
Wani Bidiyo ya bayyana inda aka ji shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila yana bayar da umarnin a lalata jam'iyyar ADC.
Ya bayar da umarni ne ga dan majalisa daga jihar Kogi, Leke Abejide.
An ga Bidiyon ya watsu sosai a kamafafen sada zumunta inda lamarin ya bayar da mamaki.
https://twitter.com/i/status/2046234845865476183
Rahotanni sun bayyana cewa, Tsaffin 'yansandan dake zanga-zangar neman hakkinsu a Abuja sun tare babbar kofar shiga fadar shugaban kasa, Aso Villa dake Abuja.
Tsaffin 'Yansandan sun nemi cewa sai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa dokar da zata fitar da su daga tsarin Fansho na gama gari sannan zasu bar wajan.
'Yansandan dai sun kwashe kwanaki suna zanga-zangar dan neman a biya musu hakkokinsu na kammala aiki.
https://twitter.com/i/status/2046196575051952590
Farashin dala a kasuwar Gwamnati ta yau, Litinin 20, ga watan Aprilu na shekarar 2026 ya kama akan Naira 1,347.33 duk wata.
A kasuwar bayan fage ta garuruwan Kano, Legas da Abuja kiwa ana sayen dalar akan Naira 1,395, inda ake sayar da ita akan Naira 1405
Wani malami da ya je koyar da dalibai a jami'ar Federal University Kashere dake jihar Gombe ya bayyana cewa ya je ya iske ajin ba kowa.
Ya dauki Bidiyon ajin inda aka ga kujeru inda yace zai koma ofis ya tafi gida.
https://www.tiktok.com/@amedkt1/video/7630389740956634389?_r=1&_t=ZS-95gGL3UR7Wz
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta karbi bashin Naira Biliyan 100 daga asusun bankunan 'yan Najeriya wadanda ba'a amfani dasu, wanda a turance ake kira da Dormant account.
Hakanan ta dauki kudaden daga ribar kamfanoni wadda mutane masu hannun jari a kamfanonin basu karbaba wadda a turance ake kira da Dividend.
Wata dokar kudi da aka yi a shekarar 2020 ce ta baiwa Gwamnatin tarayya damar rantar irin wadannan kudade.
A dazu ne dai muka di wani Dr. Adam ya koka cewa dan takarar Gwamnan jihar Gombe, Farfesa Ali Pantami ya yi Blocking dinsa saboda ya gaya masa gaskiya a cewar Adamu
A yanzu kuwa watace itama me suna Huraira ta roki mallam ya bata Miliyan 2 ta ja jari bayan ta ganshi a jirgin sama.
Saidai itama yayi Blocking dinta.
A karshe dai ta roki malam ko dubu dari biyu ya bata.
https://twitter.com/i/status/2045896467609420011