Tuesday, May 12
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon yanda ‘yansanda suka bi sahun farar hula suka tsere yayin da bata gari suka sace akwatin zabe a wata mazaba dake jihar Ondo

Kalli Bidiyon yanda ‘yansanda suka bi sahun farar hula suka tsere yayin da bata gari suka sace akwatin zabe a wata mazaba dake jihar Ondo

Duk Labarai
A yayin zaben jihad Ondo, wani abin mamaki ya faru India aka ga masu satar akwatin zabe sun kori mutane ciki hadda jami'an 'yansanda. Bidiyon dai ya nuna yanda 'yansandan da masu zaben suna jin harbi suka tsere da guru. https://twitter.com/TrendingEx/status/1858035226699546963?t=ps2EaKGTkBs4KGNPkXb9jg&s=19 Satar Akwatin Zane ba Sabin Abu bane a siyasar Najeriya.
Ji Yanda ta kaya tsakanin Hadiza Gabon da wani da yace mata a haka zata kare ba miji

Ji Yanda ta kaya tsakanin Hadiza Gabon da wani da yace mata a haka zata kare ba miji

Duk Labarai
Taurawar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta ta saka wani hotonta inda race tana Alfahari da kanta. Da yawan masoyanta sun mata fatan Alheri, saidai kamar ko da yaushe, an samu Wanda suka gaya mata ba dadi. Wani yace mata a haka zaki kare babu miji. Inda Hadizar ta amsa da cewa, diyarkace data kare a haka. Saidai saga baya ya bayyana mata cewa yayi nadamar maganarsa inda ya bata hakuri.
Sarauniyar Kyan Najeriya ta zo ta biyu a gasar Sarauniyar Kyau ta Duniya

Sarauniyar Kyan Najeriya ta zo ta biyu a gasar Sarauniyar Kyau ta Duniya

Duk Labarai
Sarauniyar kyau ta Najeriya, Chidimma Adetshina ta zo ta biyu a gasar Sarauniyar kyau ta Duniya da aka kammala a gasar Mexico. Sarauniyar kyau ta Najeriya da ta kasar Denmark ne suka kai Karshen gasar bayan doke sauran matan da suka kara dasu. Saidai a karshe, Sarauniyar kyau ta kasar Denmark CE ta lashe gasar inda ta Najeriya ta zo ta biyu. Saidai duk da haka an bayyana Sarauniyar kyau ta Najeriya a matsayin gwarzuwa wadda ta nuna bajinta sosai a gasar. Da Safiyar ranar Lahadi be aka kammala gasar wadda aka Dade ba'a yi me armashi da daukar hankali irinta ba.
Addu’o’in mu ne yasa darajar Naira bata fadi aka rika sayar da dala daya akan Naira dubu 10,000 ba>>Inji Pasto Adebayo

Addu’o’in mu ne yasa darajar Naira bata fadi aka rika sayar da dala daya akan Naira dubu 10,000 ba>>Inji Pasto Adebayo

Duk Labarai
Babban Fasto na cocin (RCCG), Fasto Adebayo ya bayyana cewa addu'o'in da suke da taimakon Allah ne yasa darajar Naira bata fadi ba aka rika sayen dalar Amirka daya akan Naira dubu 10 ba. Tun bayan da Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta cire tallafin dala ne farashin dalar yayi tashin gwauron zabi zuwa sama da Naira 1,600. Hakan ya taimaka wajan hauhawar farashin kayan masarufi.
‘Yansanda sun kama masu gàrkùwà da mutane a Kano

‘Yansanda sun kama masu gàrkùwà da mutane a Kano

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Kano sun kama masu laifi gida 82. An kamasu ne tsakanin Nov. 1 zuwa Nov. 14. Wanda aka kama din ana zarginsu da aikata laifukan kwacen waya, garkuwa da mutane da safarar kwaya. Kakakin 'yansandan jihar, Abdullahi Kiyawa ne ya bayyana haka a hedikwatar 'yansandan jihar dake Bompai Kano. Ya bayyana cewa sun samu wannan nasara ne bayan wasu dabaru da suka fito dasu na kama masu laifi. Yace sun kwace makaman Bindiga AK 47 guda daya da bindigu kirar gida guda 3 da adduna da wukake guda 30 sai miyagun gwayoyi da sauransu. Ya bayar da tabbacin ci gaba da kokarin kawo zaman lafiya a jihar da yaki da aikata miyagun laifuka.
Karya ake mana, bamu ce mun daina siyo man fetur daga kasar waje ba>>NNPCL

Karya ake mana, bamu ce mun daina siyo man fetur daga kasar waje ba>>NNPCL

Duk Labarai
Kamfanin man fetur na kasa,NNPCL ya musanta Rahotannin dake cewa ya daina shigo da tataccen man fetur daga kasashen waje inda a yanzu yake sayen man daga matatar man fetur ta Dangote. Labarai sun yadu dai cewa NNPCL tace ta daina shigowa da man fetur daga kasashen waje. Saidai a sanarwar da kakakin NNPCL din Mr Femi Soneye ya fitar yace wannan rahoto ba gaskiya bane. Yace suna dubawane su ga idan shigo da man fetur din daga kasar waje yafi sauki to daga wajen zasu siyo idan kuma sayenshi a gida yafi sauki to sai su siya a gida. Yace lamarin labarin cewa sun daina shigo da man fetur ba gaskiya bane inda ya jawo hankalin 'yan jarida da su rika yin bincike kamin watsa labaransu.