Sunday, June 28
Shadow
Kalli Bidiyon: Rahotannin tsaro dake kawowa daga Zamfara duk karyane, yau gani a Dajin Zamfara ba sauran wata matsalar tsaro, Bello Matawalle ya gama dasu>>Inji Usman A. Adams

Kalli Bidiyon: Rahotannin tsaro dake kawowa daga Zamfara duk karyane, yau gani a Dajin Zamfara ba sauran wata matsalar tsaro, Bello Matawalle ya gama dasu>>Inji Usman A. Adams

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Usman A. Adams yayi ikirarin cewa, matsalar tsaron da ake kawowa daga jihar Zamfara karyace. Yace Karamin ministan tsaro, Bello Matawalle ya gama da duk wata matsalar tsaro. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo inda aka ganshi a wani daji da yace dajin jihar Zamfara ne kuma gashi ya je babu kowa a ciki. Yace Bidiyon da ake yadawa a kafafen sada zumunta abubuwan dake faruwane a kasashen Sudan, Mali, da Somalia. https://www.tiktok.com/@horonzango/video/7649125694554819848?_r=1&_t=ZS-974FWcxuZBk
Gawunane ya zo wajan mu dan mu bashi takarar gwamna, bamu muka nemeshi ba>>Inji jam’iyyar ADC

Gawunane ya zo wajan mu dan mu bashi takarar gwamna, bamu muka nemeshi ba>>Inji jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC reshen jihar Kano ta tabbatar da cewa yanzu haka ganawa na ci gaba da gudana a tsakaninta da Nasiru Yusuf Gawuna. Shugaban jam'iyyar a jihar, Musa Ungogo ne ya bayyana haka ga manema labarai na jaridar Punchng. Yace gawuna ya aika musu da wakilansa da suka hada da tsohon shugaban karamar hukumar Kumbotso, Alhaji Sagir Fanshekara da Hon Kadawa inda suka ce Gawuna na son komawa jam'iyyar. Amma sai an masa alkawarin za'a bashi takarar Gwamna ba tare da hamayya ba sannan a baiwa wasu daga cikin mutanensa mukamai. Ungogo yace sun bukaci Gawuna da ya rubuto musu da bukatunsa a rubuce su duba suga yiyuwar hakan. Yace labaran da ake yadawa a kafafen sadarwa cewa wai sune suke nemansa kuma sun masa alkawarin tikitin takarar gwamna da kudin yakin neman zabe ba gaskiya...
Kalli Bidiyon: Ba Tinubu nake nufi ba>>Inji Matarnan da aka ga tana cewa, ko da kudi ko babu zasu zabi Jagaban

Kalli Bidiyon: Ba Tinubu nake nufi ba>>Inji Matarnan da aka ga tana cewa, ko da kudi ko babu zasu zabi Jagaban

Duk Labarai
Matarnan da ta dauki hankula a kafafen sada zumunta inda aka jita tana cewa, ko da kudi ko babu zasu zabi Jagaban. Ta fito tace ba da Tinubu take ba. Tace da wani Jagaba Isa take. Bidiyon nata na farko dai ya dauki hankuka inda da dama suka rika sukarta da mata fatan abubuwa daban-daban. https://twitter.com/i/status/2064101006330282483
Kalli Bidiyon: Idan ina son kudi, kawai zan daga wayane in Kira shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu >>Inji Babachir David Lawal

Kalli Bidiyon: Idan ina son kudi, kawai zan daga wayane in Kira shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu >>Inji Babachir David Lawal

Duk Labarai
Tsohon sakataren Gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal ya bayyana cewa ba siyasar kudi yake yi ba. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace ba gaskiya bane cewar da ake wai Hayatu-Deen ya bashi kudi dan ya taimaka masa ya ci zaben fidda gwani na dan takarar jam'iyyar ADC. Yace Hayatu-Deen bashi da kudin da zai bashi a yanzu. Yace idan yana son kudi, waya kawai zai daga ya kira shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kuma ya tabbatar kamin ya je gida kudin zasu shiga asusunsa. https://twitter.com/i/status/2064070173968011711
Kalli Bidiyon: Dakin da muke tsare masu laifi akwai na’urar sanyaya daki, AC, sannan akwai Talabijin ana kallon Premier League da labarai>>Inji Kwamishinan ‘yansandan Abuja

Kalli Bidiyon: Dakin da muke tsare masu laifi akwai na’urar sanyaya daki, AC, sannan akwai Talabijin ana kallon Premier League da labarai>>Inji Kwamishinan ‘yansandan Abuja

Duk Labarai
Wani Bidiyo na Kwamishinan 'yansandan babban birnin tarayya, Abuja yana cewa masu laifi da suke tsare dasu suna jin dadi ya dauki hankula. An ganshi yana cewa, a dakin da suke tsare da masu laifin akwai na'urar sanyaya daki watau AC, sannan akwai Talabijin inda ake kallon gasar Premier League da labarai. https://twitter.com/i/status/2064083533476360550 Saidai da yawa sun yi shakkun wannan ikirari nasa.