Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya taka rawa a wajan kaddamar da gyaran da akawa babban dakin taro na kasa da kasa.
A yayin kaddamarwar ya taka rawa.
Kuma an sakawa dakin taron sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
https://twitter.com/channelstv/status/1932465426044236257?t=qnSAyxARa3IcYTrLTu6Ffw&s=19
Lamarin ya dauki hankula inda wasu suka yaba, wasu kuwa kushewa suka yi.
Wannan wani fasto ne da ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan cewa, Kiristoci ne ya kamata su rika layya ba musulmai ba.
A cikin bidiyon wa'azinsa a cocinsa, Faston ya bayyana tarihin layyar inda yace sune suka fi alaka da ita ba musulmai ba.
https://twitter.com/AsakyGRN/status/1931978207919542634?t=dPTtS3iOFejah7DlOGZ87w&s=19
Wasu dai sun yadda dashi inda wasu suka ce basu yadda ba.
Fasto Jeremiah Omoto Fufeyin ya bayyana cewa, ya samar da wata riklgar bacci ga mata wadda ko likita yace maniyyin mijinki ya tsinke, to idan kika saka rigar sai kin dauki ciki.
Faston ya bayyana rigarne a cocinsa inda aka ganta dauke da hotunansa.
https://twitter.com/dammiedammie35/status/1932178002495807492?t=3BXzkL3hLAI2kAiCZoVvgQ&s=19
Lamarin ya zowa mutane da mamaki matuka.
Ministan ayyuka, David Umahi ya bayyana cewa saboda yaddar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya masa, idan ya ci amanarsa ya zama shedan.
Umahi yace Tinubu ya bashi aikin sayo kayan wani aiki da za'a yi da kudin suka kai Naira Tiriliyan 1.6, yace amma abin mamaki Tinubun bai taba kiransa ya ji ko ya ake ciki ba.
Umahi yace na kowane zai iya maka wannan abin ba dan haka shi ya fada har a gaban Tinubu cewa, daga Allah sai shi a wadanda yake girmamawa dan yafi iyalansa.
Umahi ya bayyana hakane a Abakaliki yayin ganawa da manema labarai.
Wannan wata budurwace data aikawa kawarta da Miliyan 6 ta sayo mata da jakunkuna daga kasar China.
https://twitter.com/ChuksEricE/status/1932439373796024600?t=QekclgWoU8diB80kAAua1g&s=19
Saidai ta aiko mata da kwali babu komai a ciki, lamarin yasa ya fashe da kuka tana fadin gaba daya kudinta ne ta aika mata.
Tsohon Ministan Matasa da Cigaban Wasanni, Solomon Dalung, ya ce ‘yan siyasar da suka fice daga jam’iyyun adawa zuwa jam’iyyar APC mai mulki suna yi ne kawai domin neman a share laifukansu ne na almundahana.
Dalung wanda ya bayyana hakan ne a Abuja inda ya nuna rashin gamsuwarsa da cewa ’yan siyasa suna tururuwa zuwa jam’iyyar APC ne saboda ta yi aiki mai kyau, ko dan farin jininta da yi wa talaka aikin da ya dace.
Dalung ya ce masu sauya shekar suna la'akari da kalaman tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole da ya ce komai girman zunubansu, za a gafarta musu da zarar sun koma APC, ko da yake Oshiomhole ya musanta wannan magana da aka danganta shi da ita.
Maganar gaskiya Tinubu na ƙoƙari wajen gyaran tattalin arzikin ƙasa kuma ya cancanci a ƙarfafi Gwiwarsa - Fayose.
Ayodele Fayose, tsohon gwamnan jihar Ekiti, ya ce ziyararsa ga Shugaba Bola Tinubu ta kasance ta kashin kai ne domin ƙarfafa masa gwiwa.
“Ziyarata na kashin kai ce, domin ƙara ƙarfafa shi ya cigaba da abin da yake yi domin ‘yan Najeriya. Babu wanda ya ce abu ne mai sauƙi, amma babu wani mu’ujiza da zai iya sauya lamura cikin dare ɗaya,” in ji Fayose ga manema labarai a Legas ranar Litinin bayan ganawarsa da shugaban ƙasa.
Ya ce Tinubu ya cancanci yabo bisa ƙoƙarinsa har zuwa yanzu.
“Amma saboda abinda shugaban ƙasa ya riga ya yi, dole ne mu yaba masa,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya ce tarihin sukar da ya yi wa gwamnatoci baya bai hana shi gane irin ƙoƙarin Tin...
In da na ci zaɓe nima sai na cire tallafin man fetur amma ba farar-ɗaya irin na Tinubu ba - Obi
Peter Obi, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, ya ce da ya ci zaɓen da shi ma sai ya cire tallafin man fetur kuma ya kyale Naira ta neman wa kan ta daraja, kamar sai yadda shugaba Bola Tinubu ya yi.
Da ya ke magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise a jiya Litinin, Obi ya ce da zai aiwatar da manufofin a hankali a hankali ba farar-ɗaya ba gaba-gaɗi irin na Tinubu ba.
Tsohon gwamnan na Anambra ya ce kowa ya san cewa dole ne a kawo karshen "baƙala da cin hanci da rashawa" da ke tattare da tsarin tallafin man fetur.
Obi ya yi tambaya kan inda kudaden da ake tarawa cire daga tallafin man fetur suke tun lokacin da aka cire shi, ya kara d...