Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya sauke Ministan Kudi da Ministan gidaje
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Ministan Kudi, Wale Edun da Ministan Gidaje Da ci gaban birane Umar Dangiwa.
Sakataren Gwamnati, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An baiwa Wale Edun umarnin ya mikawa karamin Ministan kudi, Mr. Taiwo Oyedele ragamar ma'aikatar.
Hakanan shugaba Tinubu ya nada Mr. Muttaqha Rabe Darma (PhD) a matsayin Ministan Gidaje da ci gaban birane.








