Sunday, April 19
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Abinda Peter Obi yayi bayan da aka fara sallar Gawar Mahaifiyar Malam Nasiru Ahmad El-Rufai shi kuma yana cikin masallacin

Kalli Bidiyon: Abinda Peter Obi yayi bayan da aka fara sallar Gawar Mahaifiyar Malam Nasiru Ahmad El-Rufai shi kuma yana cikin masallacin

Duk Labarai
Peter Obi yana cikin babban masallacin Juma'a na Abuja yayin da aka kabbara sallar gawar mahaifiyar malam Nasiru Ahmad El-Rufai. An hango Peter Obi tsaye a cikin masallacin inda ya kalli kudu yayin da Musulmai suka kalli gabas suna sallar Lamarin ya dauki hankula a kafafen sadarwa. https://twitter.com/i/status/2038293691316507019
Allah Sarki kalli Bidiyon yanda Farfesa Isa Ali Pantami ya shirya Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani da tsohon Gwamnan Jihar  Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a wajan jana’izar mahaifiyarsa

Allah Sarki kalli Bidiyon yanda Farfesa Isa Ali Pantami ya shirya Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani da tsohon Gwamnan Jihar Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a wajan jana’izar mahaifiyarsa

Duk Labarai
Babban malamin addinin Islama, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya shirya gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani da tsohon Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Yayi wannan shiri ne a wajan jana'izar mahaifiyar El-Rufai da aa yi a Kano. An ga yanda yasa suka gaisa uwa yace su yafewa juna. https://twitter.com/i/status/2038282643507183811 https://www.tiktok.com/@hon.gkata/video/7622761880288791829?_r=1&_t=ZS-956RDpVMplp&sp_source=7537614245375297080
Na sadaukar da Albashina gaba daya tun daga farkon hawan mulkina a baiwa Iyalan sojojin da suka rigamu gidan gaskiya da kuma wanda suka jikata>>Inji Shugaba Tinubu

Na sadaukar da Albashina gaba daya tun daga farkon hawan mulkina a baiwa Iyalan sojojin da suka rigamu gidan gaskiya da kuma wanda suka jikata>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, ya sadaukar da Albashinsa gaba daya tun daga hawansa mulki a 2023 zuwa ga iyalan sojoji da suka rigamu gidan gaskiya da kuma wadanda suka jikkata. Shugaba Tinubu yace an bude wani asusu ne na musamman dan tallafawa irin wadannan sojoji da iyalansu, kuma shine shi ya fara saka tasa Gudummawar. Yace yana kira ga Gwamnoni, Sanatoci da sauran 'yan kasuwa da abokan sa suma su saka nasu gudummawar. Ya bayyana cewa aikin na sojoji sadaukarwa ce wadda bai kamata a barta haka ba.
Dole kowa ya gayawa Gwamnati yawan kudaden da yake samu kuma ya biya haraji nan da 31 Maris

Dole kowa ya gayawa Gwamnati yawan kudaden da yake samu kuma ya biya haraji nan da 31 Maris

Duk Labarai
Tarar Naira dubu Dari(100,000) ce duk wanda bai gayawa Gwamnati yawan kudin da yake samu ba sannan ya biya haraji nan da ranar 31 ga watan Maris zai biya. Dokar tace kamin nan da ranar 31 ga watan Maris dolene kowane dan Najeriya ya gayawa Gwamnati yawan kudaden da yake samu sannan ya biya Haraji. Hakanan dokar tace duk wanda bai yi hakan ba za'a ci shi tarar Naira dubu dari(100,000) sannan za'a ci gaba da cinsa tarar Naira dubu hamsin(50,000) kowane wata da yaki fadawa Gwamnati yawan kudaden da yake samu kuma yaki biyan Haraji Yanda mutum zai gayawa Gwamnati yawan kudaden da yake samu shine: Ka samu Lambar biyan Haraji da ake cewa TIN. Ka Shiga E tax portal na jiharka. Saika cie duka bayanan da ake da bukata.
Kalli Bidiyon yanda aka bugawa mutanen da suka je babban taron jam’iyyar APC a Abuja Hayaki me sa hawaye

Kalli Bidiyon yanda aka bugawa mutanen da suka je babban taron jam’iyyar APC a Abuja Hayaki me sa hawaye

Duk Labarai
Wannan Bidiyon ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta bayan da aka ga wanda suka je taron jam'iyyar APC na kasa a Abuja an buga musu barkonon Tsohuwa. Da yawa dai sun rika musu Allah ya kara. https://www.tiktok.com/@italoo.jesus.1111/video/7622266775413083399?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7622266775413083399&source=h5_m&timestamp=1774707469&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7606977366144993025&share_link_id=f9b38912-d2ce-4aea-a5b2-69b91dd57ffc&share_app_id=123...
Ban yi zaman banza ba a hannun ICPC, Kullun Azumi nike sannan na sauke Qur’ani>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Ban yi zaman banza ba a hannun ICPC, Kullun Azumi nike sannan na sauke Qur’ani>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wani na hannun damar malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana irin zaman da yayi a hannun ICPC bayan da suka kamashi. Ya bayyana cewa malam har zuwa jiya da aka sakeshi azumi ya rika yi a hannun ICPC. Kuma ya sauke Qur'ani hakanan ya karanta litattafai da dama kuma ya rubuta wasu. A jiyane dai ICPC suka bayar da Belin shi bayan rasuwar mahaifiyarsa.
Kalli Bidiyon: Ya halatta idan mutun ya je neman Aure ya ga ko ina a jikin matar da zai aura amma banda gabanta>>Inji Asadussunnah

Kalli Bidiyon: Ya halatta idan mutun ya je neman Aure ya ga ko ina a jikin matar da zai aura amma banda gabanta>>Inji Asadussunnah

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Malam Musa Asadussunnah ya bayyana cewa akwai fatawoyi akan guraren da ya kamata mutum ya kalla a jikin matar da zai aura. Yace wata fatawar tace idan mutum ya je wajan matar da zai aura ta saka Hijabi, da Niqabi da safar hannu data kafa. Yace wata fatawar kuma tace zai iya ganin ko ina in banda gaban matar. Danna nan dan kallon Bidiyon jawabin malam