Saturday, May 16
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: An bayyana yawan kudaden da ake zargin an baiwa Nafiu Bala dan ya kawo tarnaki a jam’iyyar ADC

Da Duminsa: An bayyana yawan kudaden da ake zargin an baiwa Nafiu Bala dan ya kawo tarnaki a jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Wasu Rahotanni sun yi zargin cewa kudi aka baiwa Nafiu Bala Gombe da yake ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC har ma ya kai su Atiku Kotu. Rahotan yace an baiwa Nafiu Naira Biliyan 2 ne ya kawo wannan rikici a cikin jam'iyyar ADC. Hakanan rahoton yace Nafiu yanzu ya fara buya baya shiga cikin mutane sosai. A ranar 7 ga watan Afrilu ne dai ake sa ran sake komawa kotu dan ci gaba da shari'ar ta ADC inda ake tsammanin su Atiku zasu nemi kotun ta yi watsi da karar. https://twitter.com/i/status/2040658724059009259
Ji Abinda Arteta yace bayan da Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton

Ji Abinda Arteta yace bayan da Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton

Duk Labarai
Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton da ci 2-1 wanda ya fitar da ita daga gasar cin kofin FA Cup. A martaninsa bayan wasan, Kocin Arsenal Arteta ya bayyana cewa, ba zai soki yaransa ba. Yace sun shafe watanni 9 suna kokari ma kungiyar dan sun yi rashin nasara a wannan wasan ba zai sokesu ba, yace amma shine ya dauki alhakin wannan rashin nasara.
Da Duminsa: Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da Seyi Makinde na Oyo da wasu ‘yan majalisar tarayya sun fasa komawa jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da Seyi Makinde na Oyo da wasu ‘yan majalisar tarayya sun fasa komawa jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Muhammad da Takwaransa na jihar Oyo, Seyi Makinde sun fasa shirinsu na komawa jam'iyyar ADC. Rahoton jaridar Punchng ya bayyana cewa, Gwamnonin sun dakatar da aniyarsu ne biyo bayan cite sunayen shuwagabannin ADC da INEC ta yi daga kundin tattara bayananta. Hakanan Wasu 'yan majalisar tarayya dake shirin komawa jam'iyyar ta ADC suna sun fasa saboda wannan rikicin da ya mamaye jam'iyyar ta ADC. INEC ta sanar da cewa, zata jira sai bayan hukuncin kotu kamin su yanke shawara kan shuwagabannin jam'iyyar ADC.
Kalli Bidiyon: Na yi Ministan wutar Lantarkin na tara kudi iya kudi ta yanda ko da ban sake neman wani mukamin siyasa ba bazan yi talauci ba>>Inji Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu

Kalli Bidiyon: Na yi Ministan wutar Lantarkin na tara kudi iya kudi ta yanda ko da ban sake neman wani mukamin siyasa ba bazan yi talauci ba>>Inji Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu

Duk Labarai
A wani Bidiyo dake ta yawo a kafafen sada zumunta an ga Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu yana bayyana cewa ya tara kudi. Ta yanda ko da bai sake neman wani mukamin gwamnati ba ba zai yi talauci ba. https://twitter.com/i/status/2040503475293851651
Kalli Hotun da Bidiyon: Irin kyakkyawar tarbar da Gwamna Abba ya samu a Kano bayan dawowa daga babban taron APC na kasa

Kalli Hotun da Bidiyon: Irin kyakkyawar tarbar da Gwamna Abba ya samu a Kano bayan dawowa daga babban taron APC na kasa

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya samu kyakkyawar tarba bayan da ya koma Kano biyo bayan halartar babban taron jam'iyyar APC na kasa da aka yi a Abuja. Dubun dubatar mutanene suka taru sukawa Abba barka da dawowa Inda shi kuma ya fito ta saman mota yana amsa gaisuwa. Wasu rahotanni sun ce har kusan 9 dare Gwamna bai samu shiga gida ba saboda taron jama'a. https://twitter.com/i/status/2040520731356774667
Ya kamata duk malami ko faston dake tallar Tinubu mutane su rika musu na Jqkiy>>Inji dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Ya kamata duk malami ko faston dake tallar Tinubu mutane su rika musu na Jqkiy>>Inji dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Duk Labarai
Dan gidan tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai ya bayyana cewa, ya kamata duk malami ko faston dake kira a zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mutane su rika musu na jqkiy. Ya bayyana hakane a shafinsa na X, wani ne ya rubuta hakan inda shima Malam Bashir yace ya amince da wanann mataki. https://twitter.com/i/status/2040266110017179700
Nafiu Bala wanda ya kai Su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, Peter Obi Kotu yace shine shugaban APC amma suna son yi masa kwace, ya aikawa kasar Amurka Takardar korafi

Nafiu Bala wanda ya kai Su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, Peter Obi Kotu yace shine shugaban APC amma suna son yi masa kwace, ya aikawa kasar Amurka Takardar korafi

Duk Labarai
Nafiu Bala Gombe wanda ke ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC kuma ya maka su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi a kotu yace suna son rabashi da mukaminsa ta hanyar karfa-karfa ya aikawa kasar Amurka da korafi. Nafiu ya ce a cikin takardar a dokar jam'iyyar ADC, idan shugaba ya sauka mataimakinsa ne ke karbar shugabancin jam'iyyar, yace dan haka da tsohon shugaban jam'iyyar ya sauka, Shine halastaccen shugaba. Saidai yace su Atiku, El-Rufai, Kwankwaso, da Peter Obi sun je sun masa karfa-karfa. Yace suna zargin wai shugaban kasa ne ko jam'iyyar shugaban kasa ce ta dauki nauyinsa amma yace ba gaskiya bane bashi da alaka da APC ko shugaban kasa. Yace dan haka yana kira ga kasar Amurka data hana wadannan mutane shiga kasarta.
Kalli Bidiyon: Idan na ci gaba da magana ba zamu iya barin garinnan ba kuma ba ku da inda zamu iya kwana>>Shugaba Tinubu ya gayawa al’ummar Jos inda ya yanke maganar da yake

Kalli Bidiyon: Idan na ci gaba da magana ba zamu iya barin garinnan ba kuma ba ku da inda zamu iya kwana>>Shugaba Tinubu ya gayawa al’ummar Jos inda ya yanke maganar da yake

Duk Labarai
A ziyarar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai jihar Filato an jiyoshi yana cewa babu lokaci, idan ya ci gaba da magana, ba lallai su iya komawa Abuja ba. Ya kara da cewa kuma a Jos babu inda zasu iya kwana, inda ya karkar maganarsa da wannan kalamai ya zauna. https://twitter.com/i/status/2040364555398787567 Wannan kalamai nasa dai sun jawo cece-kuce inda ake ganin basu dace ba. A baya dai shugaban yace garin Jos ba wutar lantarki inda yace kuma mintuna goma zasu yi su koma. Shugaban yaki shiga cikin garin Jos inda a filin jirgi ya tsaya saidai aka kai masa iyalan wadanda suka jikkata ya gana dasu a filin Jirgin. Hakan ya jawo masa suka sosai cikin wadanda suka sokeshi hadda tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar. Saidai fadar shugaban kasa tace, shug...
Kalli Bidiyon: Kada wanda ya karya doka ko ya tayar da rigima saboda wani dan siyasa, Ba zaka ga yaran masu kudi irina muna haka ba>>Inji Hon Bello El-Rufai, dan tsohon Gwamnan Kaduna

Kalli Bidiyon: Kada wanda ya karya doka ko ya tayar da rigima saboda wani dan siyasa, Ba zaka ga yaran masu kudi irina muna haka ba>>Inji Hon Bello El-Rufai, dan tsohon Gwamnan Kaduna

Duk Labarai
Hon. Bello El-Rufai da a wajan tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi kira ga matasa kada su karya doka ko su tada rigima saboda wani dansiyasa. Yace ba zaka ga 'ya'yan masu kudi irinsa suna hakan ba. Wannan magana tasa ta jawo cece-kuce inda wasu suka goyi bayansa wasu kuma suka sokeshi. https://twitter.com/i/status/2040444856384844169