Thursday, May 22
Shadow

Duk Labarai

Ko da taimakonku ko babu zamu ci gaba da Yàkì sai mun ga bayan Kungiyar Hàmàs>>Netanyahu ya mayarwa da Amurka Martani kan kiran da ta mai ya daina Kàshè Falasdiynawa

Ko da taimakonku ko babu zamu ci gaba da Yàkì sai mun ga bayan Kungiyar Hàmàs>>Netanyahu ya mayarwa da Amurka Martani kan kiran da ta mai ya daina Kàshè Falasdiynawa

Duk Labarai
Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu ya bayyanawa kasar Amurka cewa ko da ita ko ba taimakonta zai ci gaba da yaki a Gaza. Hakan na zuwane bayan da Dangantaka ke kara yin tsami tsakanin Amurka da Israyla. Rahotanni sun ce shugaban Amurka, Donald Trump na matsawa Benjamin Netanyahu akan ya dakatar da yakin amma sai ma kara kaimi yake. Hakanan shuwagabannin kasashen Turawa ma sun fara nuna rashin goyon bayansu ga yakin inda suka gargadi Netanyahu amma duk yayi kunnen uwar shegu.
Gwanin Ban Tausai: Ji Yanda ‘yan Achaba sukawa wani Bakanike kìsàn gilla a Sule ja saboda ya buge wani me Achaba dan Uwansu ya ji Rauni

Gwanin Ban Tausai: Ji Yanda ‘yan Achaba sukawa wani Bakanike kìsàn gilla a Sule ja saboda ya buge wani me Achaba dan Uwansu ya ji Rauni

Duk Labarai
Rahotanni daga Suleja Jihar Naija na cewa, Wani bakanike me suna Yusuf Isiaka ya gamu da fushin wasu 'yan Achaba bayan da ya buge wani daga cikinsu har ya ji rauni. Rahoton yace Yusuf yana gida sai me gidanshi ya kirashi ya bashi mota ya je ya gyara masa. Yana kan hanya ne sai ya buge wani dan Achaba wanda a cewar Rahoton dan Achabar ne ya fado masa, dan Achabar yaji rauni. Anan ne 'yan Achaba suka rufar masa da zagi da duka inda daga baya aka sasantasu, yace zai kai kara wajan 'yansanda. Ya hau mota ya ci gaba da tafiya kawai sai ya ji ana ihu Barawo, 'yan Achaba da yawa a bayansa, ganin yawansu yasa bai tsaya ba ya ci gaba da tuki inda su kuma suka ci gaba da binsa suna kara yawa sai da suka kai 50. A karshe sun cin masa suka fiddoshi daga mota suka dakeshi har ya mutu. ...
Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì

Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì
Shekara daya bayan da Gwamnatin Tinubu tace an gyarasu ‘Har yanzu matatun man fetur na Fatakwal da Wari basu fara fitar da man fetur ba’

Shekara daya bayan da Gwamnatin Tinubu tace an gyarasu ‘Har yanzu matatun man fetur na Fatakwal da Wari basu fara fitar da man fetur ba’

Duk Labarai
Masu hada-hadar man fetur a Najeriya na kokawa kan yadda suke samun matsala wajen samun fetur daga matatun gwamnati guda biyu da aka gyara kwanan nan—matatar Fatakwal da na Warri—shekara daya bayan da aka bayyana cewa sun fara aiki. Najeriya, wadda ta shafe shekaru tana fama da ƙarancin man fetur, ta kashe kimanin dala biliyan 2.4 tun daga shekara 2021 domin farfaɗo da waɗannan matatun da ke yankin Niger Delta, da nufin dakatar da dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje. Sai dai har yanzu, ba su fara fitar da man fetur ba. Kungiyar 'yan kasuwa masu gidajen mai ta Najeriya, PETROAN, ta bayyana wa kamfanin dillancin labaran Reuters cewa sama da mambobinta 6,700 har yanzu na dogaro da shigo da mai daga waje da kuma matatar Dangote. Bisa bayanan ƙungiyar, har zuwa watan Maris ...
Dokar tilastawa ‘yan Najeriya su rika yin zabe ba zata yi aiki ba>>Inji Femi Falana SAN

Dokar tilastawa ‘yan Najeriya su rika yin zabe ba zata yi aiki ba>>Inji Femi Falana SAN

Duk Labarai
Babban Lauyan Najeriya, Femi Falana, SAN ya bayyana cewa, dokar tilastawa 'yan Najeriya sai sun yi zabe ba zata yi aiki ba. Majalisar wakilai ta fara tattaunawa akan wani kudirin doka da kakakin majalisar, Tajuddeen Abbas ya gabatar da ya bukaci kowace dan Najeriya me hankali dole ya rika yin zabe. Dokar dai har ta tsallake karatu na 2. Saidai a nasa jawabin, Femi Falana yace wannan doka ba zata yi aiki ba. Yace dokar Najeriya ta tanadi a baiwa dan Najeriya damar ya yi tunani akan wanda zai zaba sannan doka ta bashi damar ya boye wanda ya kadawa kuri'ar. Yace dan haka wannan doka ba zata yi aiki ba duk da yasan cewa ana kokarin zartas da itane dan karfafawa mutane yin zabe.
Daliba ‘Yar Shekara 15 Ta Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina Na Wucin-Gadi Na Tsawon Mintuna Biyar

Daliba ‘Yar Shekara 15 Ta Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina Na Wucin-Gadi Na Tsawon Mintuna Biyar

Duk Labarai
Daliba 'Yar Shekara 15 Ta Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina Na Wucin-Gadi Na Tsawon Mintuna Biyar Daga Comr Nura Siniya Shugaban majalisar dokokin jihar Katsina Hon. Nasiru Yahaya Daura, ya miƙa ragamar shugabancin majalisa na minti 5 ga wata ɗaliba mai hazaƙa Marwa Nasir Yahaya, a lokacin da daliban makarantar suka kawo ziyarar duba ayyukan majalisar, domin sanin makamar aiki, a ranar Litinin 19 ga watan Mayu 2025. Katsina Reporters ta samu cewa, daliban makarantar “Little Angel ne suka zaɓi Marwa Nasir Yahaya, saboda kwazonta ga harkar ilimin addini da na zamani. Ɗalibar dai ta kasance ɗiya ga shugaban majalisar dokokin na jihar Katsina.
PDP ta bayyana yanda za’a yi a kayar da Tinubu karfe dayan rana a zaben 2027

PDP ta bayyana yanda za’a yi a kayar da Tinubu karfe dayan rana a zaben 2027

Duk Labarai
Jam'iyyar PDP ta bayyana cewa hadakata tsakanin Atiku Abubakar da Peter Obi da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai baiwa 'yan adawa nasara akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027. Mataimakin shugaban matasa na jam'iyyar na kasa, Hon. Timothy Osadolor ne ya bayyanawa jaridar Vanguard hakan a wata ganawa da ta yi dashi. Yace Musamman Atiku Abubakar da Peter Obi idan suka hade kaga ana da jimullar kuri'u Miliyan 13 kenan inda shi kuma shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke da kuri'u Miliyan 8. Yace a haka tun karfe dayan rana zasu kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar zabe.
Zamu daina baka makamai da yanke duk wata hulda da kai idan ka ci gaba da Kàshè Palasdiynawa>>Shugaba Trump ya gargadi Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu

Zamu daina baka makamai da yanke duk wata hulda da kai idan ka ci gaba da Kàshè Palasdiynawa>>Shugaba Trump ya gargadi Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar White House ta kasar Amurka na cewa, shugaban kasa, Donald Trump na ci gaba da matsawa Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu akan ya dakata da yakar Falasdinawa. Rahotan yace Shugaba Trump har ta kai ga ya gayawa Benjamin Netanyahu cewa ko dai ya daina wannan yaki ko su yanke duk wata hulda dashi. Benjamin Netanyahu dai ba zai so hakan ba saboda mafi yawa kasar Amurka ce ke sayar musu da makamai. Saidai a wata majiyar an ji cewa, Benjamin Netanyahu na fadar zasu ci gaba da yakin kuma zasu samu nasara ba tare da taimakon kasar Amurka ba. Hakanan a wani Rahoto me kama da wannan, kasashen Ingila, Faransa da Canada sun yi barazanar daukar kwakkwaran mataki muddin Israela bata dakata da sabbin munanan hare-haren da take kaiwa a Gaza ba da kuma janye hana ka...
Zamu ci gaba da rage farashin Man fetur duk da yana tashi a kasuwannin Duniya >>Matatar Dangote ta sha Alkawari

Zamu ci gaba da rage farashin Man fetur duk da yana tashi a kasuwannin Duniya >>Matatar Dangote ta sha Alkawari

Duk Labarai
Matatar man Dangin ta sha Alwashin ci gaba da rage farashin Man fetur duk da yana tashi a kasuwannin Duniya. Matatar tace tana ci gaba da rage farashin man ne saboda amincewa da ta rika sayen danyen man fetur din da kudin Naira. Tace tana godiya ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya amince da yin hakan, kamar yanda wakilin matatar me suna Anthony Chiejina ya tabbatar. Matatar tace zata ci gaba da goyon bayan karfafa ci gaban tattalin arziki Najeriya da kuma tabbatar da saukin man fetur.