Friday, January 23
Shadow

Duk Labarai

Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa 9

Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa 9

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da 'ya'yansa maza da mata su 9. Katin gayyatar auren ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga cewa za'a yishi ne ranar 6 ga watan Fabrairu a babban masallacin Juma'a dake Abuja. Sunayen 'ya'yan nasa sune kamar haka, Ibrahim, Suraj, Safiya, Maryam, Aisha, Fahad, Muh’d, Nana Firdausi, and Farida. Kakakin jam'iyyar APC na jihar Zamfara, Yusuf Idris, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Duk Labarai
Wannan baiwar Allahn ta bayyana cewa ta karbi Addinin Musulunci inda ta nemi a sakata a addu'a. An ganta da litattafan Addinin Musulunci a Bidiyon data saki Kalli Bidiyon anan https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1 https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1
Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Duk Labarai
Wani sabon Bidiyon 'yan kwallon Najeriya, Super Eagles ya bayyana inda aka ji suna tattauna cewa ba'a biyasu hakkokinsu ba. An dauki Bidiyon ne kamin wasansu da Morocco wanda Moroccon ta fitar dasu a wasan Penalty. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda ake dorawa hukumar NFF alhakin hakan. https://twitter.com/i/status/2012467439267717398
Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da IBB, Obasanjo, Yakubu Gowon da sauran tsaffin Shuwagabannin Najeriya

Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da IBB, Obasanjo, Yakubu Gowon da sauran tsaffin Shuwagabannin Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta kashe Naira Biliyan 38.2 wajan kula da tsaffin shuwagabannin Najeriya a cikin shekaru 22 da suka gabata. A wannan shakerar kawai, Gwamnatin ta ware Naira Biliyan 2.3 dan kula da tsaffin shuwagabannin Najeriya. Ana dai kula da bukatun Shuwagabannin Najeriya irin su motocin hawa, kiwon Lafiyarsu, masu musu Hidima, da sauransu duk shekara.