Wednesday, September 16
Shadow
Bidiyon Dan Bello ya bankado aikin Amaja da ake yi na Titin Lagos zuwa Calabar

Bidiyon Dan Bello ya bankado aikin Amaja da ake yi na Titin Lagos zuwa Calabar

Duk Labarai
Wani Bidiyo da Dan Bello yayi ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da ya bankado badakalar aikin Titin Legos zuwa Calabar. Dan Bello yace shekaru 2 ana aikin titin amma har yanzu bai wuce Kilometre 50 ba, har yanzu ba'a ma fita daga lagos ba. Sannan yace Titin yanzu haka har ya fara lalacewa sannan ya toshe hanyar wucewar ruwa wanda hakan ya kawo ambaliyar ruwa Yace wajan Bayar da kwangilar Titin ma son rai aka yi aka baiwa wasu 'yan kasar Lebanon aikin maimakon yanda aka saba bisa al'ada kowane kamfani ya gabatar da bukatarsa a duba wanda yafi cancanta. https://twitter.com/_nonconformist1/status/2096905809288483123
Tsohon dan majalisar tarayya ya nemi EFCC ta dawo da tsohuwar binciken da takewa Atiku Abubakar

Tsohon dan majalisar tarayya ya nemi EFCC ta dawo da tsohuwar binciken da takewa Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon dan majalisaf wakilai, Hon. Ehiozuwa J. Agbonayinma ya nemi EFCC ta dawo da binciken cin hanci da rashawa na shekarar 2006 da tawa Atiku Abubakar. Ya nemi cewa ya kamata a dawo da binciken kuma a hukunta Atiku Abubakar idan an sameshi da laifi. Saidai Jaridar Leadership ta nemi jin ta bakin hukumar EFCC amma wasu ma'aikatan hukumar da sukace suna son a sakaya sunayensu, sun ce hukumar ba zata binciki Atiku Abubakar ba musamman ganin yanda lamarin yayi kusa da zaben 2027. Atiku Abubakar yace wannan maganar banzace kamata yayi Gwamnati ta mayar da hankali wajan magance matsalolin 'yan Najeriya ba yi masa bita da kulli ba.
Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Ban ce na saki Matata Maryam Nicki Minaj ba, cewa na yi ta tafi gida>>Inji Gfresh Al-amin

Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Ban ce na saki Matata Maryam Nicki Minaj ba, cewa na yi ta tafi gida>>Inji Gfresh Al-amin

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, bai ce ya saki matarsa, Maryam Nicki Minaj ba. Yace ce mata yayi ta tafi gida kawai sai ganinta yayi a Kano. Ya kuma zargi Hassan Make-Up da cewa shine ya lalata masa aure inda yace tun tana cikin gidansa, Hassan na daga cikin masu hurewa Maryak Nicki Minaj kunne cewa idan ta fito zasu aureta. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7682541538500463880?_r=1&_t=ZS-99Wvhxu26Vh
Kalli Bidiyon: Wannan matashiyar inda take cewa duk masu cewa suna sonta tasan karza suke, kawai so suke ta basu kanta

Kalli Bidiyon: Wannan matashiyar inda take cewa duk masu cewa suna sonta tasan karza suke, kawai so suke ta basu kanta

Duk Labarai
Wannan matashiyar me suna Ama ta dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan kalamanta na cewa, duk masu cewa suna sonta kawai kaya suke son su ja. Tace su fito kawai su gaya mata gaskiya. Tace hakan ba matsala bane. Wannan kalamai nata sun jawo Allah wadai. https://www.tiktok.com/@ama2s222/video/7681993427810045204?_r=1&_t=ZS-99WtTEegwOj
Kalli Bidiyon: Wani da yayi shiga irin ta Ari Baba a gidan gala suke rawar Badala da wata yarinya akace Ari babane

Kalli Bidiyon: Wani da yayi shiga irin ta Ari Baba a gidan gala suke rawar Badala da wata yarinya akace Ari babane

Duk Labarai
Wannan wanine da yayi shiga irin ta Ari Baba a gidan gala suke rawar fitsara shi da wata matashiya ana cewa wai Ari Baba ne. Saidai da yawa sun bayyana cewa ba Ari Baba bane wani ne kawai yayi shiga irin tasa. Bidiyon ya jawo cece-kuce inda aka yi Allah wadai da lamarin. https://www.tiktok.com/@imranaibrahim820/video/7682392649034124564?_r=1&_t=ZS-99WrklnzEIv
Kalli Bidiyon: Rawar Badala da  ‘yan Mata suka yi a wajan Show din Otega ta jawo Allah wadai

Kalli Bidiyon: Rawar Badala da ‘yan Mata suka yi a wajan Show din Otega ta jawo Allah wadai

Duk Labarai
'Yan mata sun yi rawar rashin tarbiyya da bada a wajan show din Otega wanda Bidiyon rawar ya karade kafafen sada zumunta. Da yawa sun rika Allah wadai da lamarin inda ake ta tattauna yanda rashin Tarbiyya tsakanin matasan Arewa ke kara kamari. https://www.tiktok.com/@danyahuza/video/7682457225515814164?_r=1&_t=ZS-99WlEcZtm2W https://www.tiktok.com/@diamond_events.ng/video/7682222461944958226?_r=1&_t=ZS-99Wko9ao7OP https://www.tiktok.com/@amstudio78/video/7682143289952193812?_r=1&_t=ZS-99WlLgGEQq5
Sukar da ake min kan riddar da dana yayi ka iya sa in bar Musulunci>>Inji Sheikh Nura Khalid

Sukar da ake min kan riddar da dana yayi ka iya sa in bar Musulunci>>Inji Sheikh Nura Khalid

Duk Labarai
A martanin da yake yi ga masu sukarsa kan komawar dansa Kirista, Sheikh Nura Khalid, Digital Imam ya bayyana cewa, wasu ma cewa suka yi dama shine ya zama Kiristan. Yace yanzu da yayi fushi a zama Kirista wace riba aka samu? Yace in banda Allah ya taimakeshi yayi zurfi a Ilimin Addinin Musulunci? https://www.tiktok.com/@shaaweuei5p/video/7682374744993205524?_r=1&_t=ZS-99WiImehRvo