Friday, April 17
Shadow
Rahotanni sun ce Hamisu Breaker ya auri Hafsat Idris

Rahotanni sun ce Hamisu Breaker ya auri Hafsat Idris

Duk Labarai
Bayan Shafe Tsawon Lokaci Suna Soyayya Daga Ƙarshe Dai Ana Raɗe-raɗin Mawaƙi Hamisu Breaker Ya Auri Jaruma Hafsat Idris Shahararren mawaƙin nan na masana’antar Kannywood, Hamisu Breaker ya auri jaruma Hafsat Idris (Ɓarauniya) bayan shafe tsawon lokaci suna soyayya a sirrance. Wasu rahotanni su bayyana cewa an ɗaura auren ne a makon da ya gabata. Idan ta tabbata, za a iya cewa ma’auratan sun shiga layin jaruman Kannywood da ke yin aure cikin sirri a baya-bayan nan. Wane fata zaku yi musu?
Tonon Silili: Tinubu ne ya dauki nauyin me son kafa kasar Yarbawa, Sunday Igboho dan ya kawowa Gwamnatin Buhari tangarda>>Inji Sowore

Tonon Silili: Tinubu ne ya dauki nauyin me son kafa kasar Yarbawa, Sunday Igboho dan ya kawowa Gwamnatin Buhari tangarda>>Inji Sowore

Duk Labarai
Mawallafin jaridar Sahara Reporters kuma me ikirarin fafutukar kare hakkin bil'adama, Omoyele Sowore ya bayyana cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne ya dauki nauyin me son kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa watau Sunday Igboho dan ya kawo matsala a gwamnatin Buhari. A wancan lokacin dai, lamari yayi kamari har sai da ta kai ga Sunday Igboho ya tsere daga Najeriya dan gujewa kamun hukumomi. Saidai a yanzu ya dawi gida Najeriya har ma ana damawa dashi a Gwamnatin Tinubu. Sowore ya bayyana hakane a wani shirin Podcast me suna Times a yayin da yake sharhi akan siyasar yankin yarbawa na Kudu maso yamma. Yace a kokarin Tinubu na samun mulki shine ya fitar da kudi aka kafa kungiyar ta son ballewa daga Najeriya a kafa kasar Yarbawa ta Oduduwa. Yace kuma Tinubu yayi hakane saboda a wa...
Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Talata

Farashin Dala a kasuwar Chanji a yau, Talata

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Latata 7 ga watan Afrilu ya kai Naira 1,379.30 akan kowace dala a kasuwar Gwamnati. A kasuwar bayan fage kuwa farashin yana akan Naira 1,379.10 akan kowace Dala. Rahoton yace farashin kasuwar Gwamnati dana kasuwar bayan fage sun zo kusan kankankan wanda hakan ke nuna kokarin gwamnati na bayar da sakamakon da ake so na daidaita farashin dalar.
Mun yi kokarin yiwa Nafiu Bala Gombe Ihisani dan ya hakura karya Kawo mana Tangarda a ADC amma ko kusa ba zamu iya bashi abinda Gwamnati ta bashi ba, dan sun bashi kudi na wuce hankali>>Inji Me Magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi

Mun yi kokarin yiwa Nafiu Bala Gombe Ihisani dan ya hakura karya Kawo mana Tangarda a ADC amma ko kusa ba zamu iya bashi abinda Gwamnati ta bashi ba, dan sun bashi kudi na wuce hankali>>Inji Me Magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi

Duk Labarai
Me magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa, sun yi yunkurin yiwa Nafiu Bala Gombe ihisani dan ya hakura kada ya kawo musu matsala a jam'iyyar ADC amma abu ya faskara. Ya bayyana cewa dalili kuwa shine ba kananan kudade da motoci da gida da jami'an tsaro Gwamnati ta bashi ba. Yace kuma da Nafiu Bala Gombe ke cewa wai bai sauka daga shugabancin ADC ba karya yake. Yace takardar da yake karyatawa yake cewa wai kwaikwayar sa hannunsa aka yi, karya yake, shine ya rubutata da kansa, sannan idan da gaske kwaikwayar sa hannunsa aka yi, me yasa bai kai korafi wajan hukuma ba dan kuwa kwaikwayar sa hannun mutum ai babban laifine. Nafiu Abdullahi dai ya maka su Atiku a kotu inda yake zargin sun masa karfa-karfa sun kwace masa shugabancin jam'iyyar ADC.
Kalli Bidiyon: Na hana wata Kirista ta musulunta bayan data samu Miji Musulmi tace min zata musulunta su yi aure>>Inji Rahama Kumo

Kalli Bidiyon: Na hana wata Kirista ta musulunta bayan data samu Miji Musulmi tace min zata musulunta su yi aure>>Inji Rahama Kumo

Duk Labarai
Rahama Kumo ta bayyana cewa wata Kirista ta kirata take ce mata zata musulunta saboda ta samu miji Musulmi yace zai aureta. Rahama wadda Tauraruwar Tiktok ce dake magana akan auratayya tace ta hana wannan kiristan karbar Musulunci. Tace dalilinta shine ta gayaa Kiristan cewa idan dai saboda wannan musulmin mijinne zata musulunta to kada ta musulunta Tace amma idan Saboda addinin musulunci ya mata ne tana son shiga to tana iya musulunta. Tace dalili shine akan yi irin wannan aure daga baya a saki matar wasu ma hadda yara wasu kuma ba'a dadewa ma abin ya zo su koma ruwa wasu kuma aita wahala dasu. https://www.tiktok.com/@rahamakumo/video/7625763829204438290?_r=1&_t=ZS-95KmYsyMFf7&sp_source=7537614245375297080
Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari’a a kotu bayan zaben 2027

Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari’a a kotu bayan zaben 2027

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari'ar bayan zaben 2027. Hakan na kunshene a cikin kasafin kudin da Gwamnatin ta aikawa da majalisar tarayya. Saidai wannan sabon tsarin na shan suka a wajan 'yan Adawa na ADC da PDP. Inda dukansu ke cewa watau sun san ma ba zasu yi adalci a zaben ba shiyasa suka shirya ma yin shari'a. Wannan dai shine karo na farko da aka ware wadannan kudade a tarihin Najeriya.
Kalli Bidiyon: Ni na maye gurbin Seyi Tinubu zan bika daji a yi dani>>Ladidi Tubeless ta gayawa Sadiq Sani Sadiq

Kalli Bidiyon: Ni na maye gurbin Seyi Tinubu zan bika daji a yi dani>>Ladidi Tubeless ta gayawa Sadiq Sani Sadiq

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ladidi Tubeless ta gayawa abokin aikinta, Sadiq Sani cewa ba ta yadda da maganar da yayi ba ta cewa dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya fito su higa daji ba. Tace salon ya musu Asara? Tace ita ta maye gurbin Seyi Tinubun idan za'a tafi dajin a tafi da ita. https://www.tiktok.com/@tubeless41/video/7625655883749494036?_r=1&_t=ZS-95K9G9Oq9qL&sp_source=7537614245375297080 Danna nan dan Kallon Bidiyon
Da Duminsa:An bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala Gombe ke shirin yiwa su Atiku da jam’iyyar ADC gobe Talata

Da Duminsa:An bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala Gombe ke shirin yiwa su Atiku da jam’iyyar ADC gobe Talata

Duk Labarai
Me magana da yawun tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar watau Paul Ibe ya bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala wanda ya kaisu kotu ke shirin yi musu gobe Talata. Yace sun samu sahihan bayanai cewa yanzu haka Nafiu Bala hana otal din Transcorp Hilton dake Abuja yana hado kan shuwagabannin jam'iyyar ADC na jihohi. Yana so ne a gobe su masa rakiya zuwa ofishin INEC suce shine shugaban jam'iyyar na kasa na gaskiya dan INEC din ta amince dashi. Ibe ya kara da cewa, Tuni Shuwagabannin jam'iyyar ADC na jihohin Abia da Edo suka goyi bayansa dan ya sayesu.