Saturday, April 18
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Na hana wata Kirista ta musulunta bayan data samu Miji Musulmi tace min zata musulunta su yi aure>>Inji Rahama Kumo

Kalli Bidiyon: Na hana wata Kirista ta musulunta bayan data samu Miji Musulmi tace min zata musulunta su yi aure>>Inji Rahama Kumo

Duk Labarai
Rahama Kumo ta bayyana cewa wata Kirista ta kirata take ce mata zata musulunta saboda ta samu miji Musulmi yace zai aureta. Rahama wadda Tauraruwar Tiktok ce dake magana akan auratayya tace ta hana wannan kiristan karbar Musulunci. Tace dalilinta shine ta gayaa Kiristan cewa idan dai saboda wannan musulmin mijinne zata musulunta to kada ta musulunta Tace amma idan Saboda addinin musulunci ya mata ne tana son shiga to tana iya musulunta. Tace dalili shine akan yi irin wannan aure daga baya a saki matar wasu ma hadda yara wasu kuma ba'a dadewa ma abin ya zo su koma ruwa wasu kuma aita wahala dasu. https://www.tiktok.com/@rahamakumo/video/7625763829204438290?_r=1&_t=ZS-95KmYsyMFf7&sp_source=7537614245375297080
Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari’a a kotu bayan zaben 2027

Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari’a a kotu bayan zaben 2027

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan 135 dan yin shari'ar bayan zaben 2027. Hakan na kunshene a cikin kasafin kudin da Gwamnatin ta aikawa da majalisar tarayya. Saidai wannan sabon tsarin na shan suka a wajan 'yan Adawa na ADC da PDP. Inda dukansu ke cewa watau sun san ma ba zasu yi adalci a zaben ba shiyasa suka shirya ma yin shari'a. Wannan dai shine karo na farko da aka ware wadannan kudade a tarihin Najeriya.
Kalli Bidiyon: Ni na maye gurbin Seyi Tinubu zan bika daji a yi dani>>Ladidi Tubeless ta gayawa Sadiq Sani Sadiq

Kalli Bidiyon: Ni na maye gurbin Seyi Tinubu zan bika daji a yi dani>>Ladidi Tubeless ta gayawa Sadiq Sani Sadiq

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Ladidi Tubeless ta gayawa abokin aikinta, Sadiq Sani cewa ba ta yadda da maganar da yayi ba ta cewa dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya fito su higa daji ba. Tace salon ya musu Asara? Tace ita ta maye gurbin Seyi Tinubun idan za'a tafi dajin a tafi da ita. https://www.tiktok.com/@tubeless41/video/7625655883749494036?_r=1&_t=ZS-95K9G9Oq9qL&sp_source=7537614245375297080 Danna nan dan Kallon Bidiyon
Da Duminsa:An bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala Gombe ke shirin yiwa su Atiku da jam’iyyar ADC gobe Talata

Da Duminsa:An bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala Gombe ke shirin yiwa su Atiku da jam’iyyar ADC gobe Talata

Duk Labarai
Me magana da yawun tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar watau Paul Ibe ya bayyana wata aika-aika da Nafiu Bala wanda ya kaisu kotu ke shirin yi musu gobe Talata. Yace sun samu sahihan bayanai cewa yanzu haka Nafiu Bala hana otal din Transcorp Hilton dake Abuja yana hado kan shuwagabannin jam'iyyar ADC na jihohi. Yana so ne a gobe su masa rakiya zuwa ofishin INEC suce shine shugaban jam'iyyar na kasa na gaskiya dan INEC din ta amince dashi. Ibe ya kara da cewa, Tuni Shuwagabannin jam'iyyar ADC na jihohin Abia da Edo suka goyi bayansa dan ya sayesu.
Ji yanda wani sabon Rikici ya kunno kai a fadar shugaban kasa dake Abuja

Ji yanda wani sabon Rikici ya kunno kai a fadar shugaban kasa dake Abuja

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Sabon Rikici ya kunno kai a fadar shugaban kasa tsakanin Sunday Dare da Daniel Bwala Rahoton yace a baya masu ruwa da tsaki a fadar shugaban kasar sun yi kuti-kuti aka kori Ajuri Ngilale daga fadar. Dalilin da yasa suka yi nasara shine dan shugaban kasar Seyi Tinubu ne ya kawoshi. Amma Shi Daniel Bwala shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne da kansa ya kirashi ya ce ya zo ya masa aiki kuma akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu. https://twitter.com/i/status/2041181867177546068
Kalli Bidiyon: Yaron Rarara ya samu karuwar da Namiji kuma saboda soyayyarsa da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya sakawa dan nasa sunan Shugaba Tinubu

Kalli Bidiyon: Yaron Rarara ya samu karuwar da Namiji kuma saboda soyayyarsa da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, ya sakawa dan nasa sunan Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Yaron Rarara, Abbani Rarara da ya samu karuwa da Namiji, ya saka masa sunan Shugaban kasa, Bola Ahmad. Daya daga cikin abokan Abbani dinne ya bayyana hakan. https://www.tiktok.com/@hon.bashirdanchiroma/video/7625288962000571669?_r=1&_t=ZS-95JYcXvQHAn&sp_source=7537614245375297080