Saturday, June 27
Shadow
Kalli Bidiyon: Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta shigarwa makarantar da ‘yata ta rasu, dan haka nima ina neman idan akwai kungiyar Musulmai nima su shigar min>>Inji Mahaifiyar Nihal

Kalli Bidiyon: Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta shigarwa makarantar da ‘yata ta rasu, dan haka nima ina neman idan akwai kungiyar Musulmai nima su shigar min>>Inji Mahaifiyar Nihal

Duk Labarai
A jiyane dai muka kawo muku rahoton wata yarinya Nihal daga Kano wadda ta rasu a makarantar kwana. Rahotannin farko sun bayyana cewa Gwale-gwale aka baiwa Nihal saboda bata yi sallah ba duk da ta gayawa malamin su cewa tana fama da rashin lafiya amma aka tilasta mata yin gwale-gwalen wanda shine yayi sanadiyyar mutuwarta. Mahaifiyar Nihal a hirar da Freedom Radio suka yi da ita tace masu makarantar sun je gida suka mata gaisuwa suka ce mata wai diyarta bata da lafiyane shine aka mata addu'a a ruwa aka bata tasha daga nan ta rasu. Tace amma sun gargadeta kada ta saurari duk wani labarin da za'a kawo mata. Tace sun kaiwa 'yansanda rahoto aka je makarantar dan zantawa da dalibai amma makarantar tace ba za'a zanta da daliban ba, inda suka iske Lauyoyi da Kungiyar Kiristoci ta Naje...
Da Duminsa: Hadiza Gabon ta saki Bidiyo a karin farko tun bayan da matar Salim Goje ta zargeta da yin soyayya da mijinta

Da Duminsa: Hadiza Gabon ta saki Bidiyo a karin farko tun bayan da matar Salim Goje ta zargeta da yin soyayya da mijinta

Duk Labarai
A karin Farko, Hadiza Gabon ta saki Bidiyo a shafinta na sada zumunta tun bayan zargin da aka mata cewa tana soyayya da Saleem Goje. Saidai ba kalar Bidiyon da ake tsammanine Hadiza Gabon ta saki ba. Da yawa zasu yi tsammanin Hadiza Gabon zata fito ta wanke kanta daga zargin da ake mata ko kuma ta fadi yanda lamura suka kasance. Saidai kawai ta ci gaba da harkokinta ne inda ta saki Bidiyon hirar da ta saba yi da jarumai. Saidai me hakan ke nufi? Wata kila shikenan ba zamu ji ainahin abinda ya faru ba ko kuma ta gaya mana bangarenta na zargin da ake mata. https://www.tiktok.com/@hadizaaliyugabon/video/7652456983181921538?_r=1&_t=ZS-97IQPF8sRxk
Da Duminsa: Davido ya kara yiwa Rarara zazzafan Martani da Hausa

Da Duminsa: Davido ya kara yiwa Rarara zazzafan Martani da Hausa

Duk Labarai
A yayin da a dazu muka kawo muku cewa, Davido ya saka kalaman da Rarara ya masa, a shafinsa na X. Inda ya rubuta cewa, Rararan ko sunansa bai iya fada ba, Debidoo yake cewa. A yanzu Davido yayiwa Rarara martani da Hausa. Ya wallafa a Story dinsa na Instagram cewa, Rarara ya kamata ya zama dan kishin kasa sannan ya daina fifita son ransa akan abinda ya shafi al'umma. Sannan ya daina zama karan farautar 'yan siyasa. Yace kuma duk mutum me kishin kasa ba zai yi shiru akan abinda ke faruwa a Najeriya ba. Davido ya kara da cewa, da ace kana da Ilimi da na tsaya na yi magana da kai, amma komai baka sani ba sakarai kawai.
Ni nasan ba zan dade a Duniya ba saboda suna neman rayuwata ruwa a jallo>>Sheikh Salihu Zaria ya fallasa wasu mugaye da suka sakoshi gaba

Ni nasan ba zan dade a Duniya ba saboda suna neman rayuwata ruwa a jallo>>Sheikh Salihu Zaria ya fallasa wasu mugaye da suka sakoshi gaba

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya bayyana cewa yasan ba zai dade a Duniya ba dan haka mutane su zama shaida ya isar da sakon Allah da ya zo dashi. Malam yace yasani cikin wadanda za'a nemi rayuwarsu akwaishi a ciki. Malam ya bayyana hakane a wajan wani majalisi da yayi me cike da taba zuciya. https://www.tiktok.com/@voiceoftheyouths_0/video/7652274408437878036?_r=1&_t=ZS-97HoMB2GsUs
Kiran da Atiku yayi cewa a saki mahaifiyata lokacin da aka sace ta cutar dani yayi>>inji Rarara

Kiran da Atiku yayi cewa a saki mahaifiyata lokacin da aka sace ta cutar dani yayi>>inji Rarara

Duk Labarai
Tauraron mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ya bayyana cewa, Kiran da Atiku Abubakar ya yi a lokacin da aka sace mahaifiyarsa cewa a saketa cutar dashi yayi. Yace suna daf da karbota sai Atiku ya wallafa a kafar sada zumunta cewa a saki mahaifiyarsa. Yace Atiku na fadin hakan sai wasu mutanen dajin suka je suka fanshi mahaifiyar tasa a hannun wadanda ke rike da ita. Yace hakan yasa aka kara daukar lokaci me tsawo kamin kubutar da mahaifiyar tasa. https://vt.tiktok.com/ZSQsF42NY
Kaddara ce kuma wannan zai iya faruwa ga kowa>>Inji Matar da maza 8 suka mata cikin shege kuma ta haifama kowannensu dan

Kaddara ce kuma wannan zai iya faruwa ga kowa>>Inji Matar da maza 8 suka mata cikin shege kuma ta haifama kowannensu dan

Duk Labarai
Matar da ta haifi yaran gaba da fatiha 8 da maza daban-daban watau kowanne yaro da mahaifinsa ta bayyana cewa kaddara ce. Matar tace ana ta maganarta a garinsu ana nunata a matsayin abin kwatance. Saidai tace hakan bai dace ba dan wannan abu ta daukeshi kaddarace kuma zata iya fadawa kan kowa. https://twitter.com/i/status/2067170298437230736