Kalli Bidiyon: Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta shigarwa makarantar da ‘yata ta rasu, dan haka nima ina neman idan akwai kungiyar Musulmai nima su shigar min>>Inji Mahaifiyar Nihal
A jiyane dai muka kawo muku rahoton wata yarinya Nihal daga Kano wadda ta rasu a makarantar kwana.
Rahotannin farko sun bayyana cewa Gwale-gwale aka baiwa Nihal saboda bata yi sallah ba duk da ta gayawa malamin su cewa tana fama da rashin lafiya amma aka tilasta mata yin gwale-gwalen wanda shine yayi sanadiyyar mutuwarta.
Mahaifiyar Nihal a hirar da Freedom Radio suka yi da ita tace masu makarantar sun je gida suka mata gaisuwa suka ce mata wai diyarta bata da lafiyane shine aka mata addu'a a ruwa aka bata tasha daga nan ta rasu.
Tace amma sun gargadeta kada ta saurari duk wani labarin da za'a kawo mata.
Tace sun kaiwa 'yansanda rahoto aka je makarantar dan zantawa da dalibai amma makarantar tace ba za'a zanta da daliban ba, inda suka iske Lauyoyi da Kungiyar Kiristoci ta Naje...







