Friday, April 17
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Gwamnatin Najeriya za ta fara yi wa mata tiyatar haihuwa kyauta

Gwamnatin Najeriya za ta fara yi wa mata tiyatar haihuwa kyauta

Duk Labarai
Ma'aikatar lafiya a Najeriya ta ƙaddamar da wani shiri na yi wa mata masu ciki tiyata kyauta a faɗin ƙasar. Shirin da aka yi wa take da Maternal Motality Reduction Innovation Initiative Mamii), an ƙaddamar da shi yayin wani taron bita na shekara-shekara a Abuja. Ministan Lafiya Muhammad Ali Pate ya bayyana shirin da zimmar rage mutuwar mata yayin haihuwa a faɗin Najeriya. "Babbar manufar wannan shiri ita ce yi wwa mata marasa ƙarfi tiyatar haihuwa kyauta, amma waɗanda suka cika ƙa'ida a asibitocin gwamnati da na kuɗi," a cewar ministan. "Ta hanyar cire matsalolin kuɗi, muna ganin babu wata mace da ya kamata a bari ba tare da an kula da ita ba ko da ba ta da kuɗi." Ya ƙara da cewa mutuwa yayin haihuwa na ci gaba da zama barazana, inda ƙananan hukumomi 172 ke haifar da kashi 5...
Abubuwa bakwai da Trump ya ce zai yi a matsayin shugaban Amurka

Abubuwa bakwai da Trump ya ce zai yi a matsayin shugaban Amurka

Duk Labarai
Donald Trump na kan hanyar komawa fadar White House bayan da ya alƙawarta kawo ƙarshen wasu matsaloli ciki har da batun 'yan cirani, da tattalin arziki, da yaƙin Ukraine. Da alama ya samu ɗimbin magoya baya sakamakon manufofinsa na siyasa, musamman a majalisar dokokin ƙasar bayan da jam'iyyarsa ta Republican ta sake ƙwace iko da majalisar dattawan ƙasar. A jawabin murnar lashe zaɓe da ya gabatar, Mista Trump ya sha alwashin ''yin mulkin bisa taken: 'Cika alƙawuran da muka ɗauka'. Amma a wasu fannonin, ya bayar da taƙaitaccen bayanin yadda zai cimma manufofin nasa. A lokacin da kafar yaɗa labarai ta Fox News ta tambaye shi a 2023, ko zai yi amfani da kujerarsa ta hanyar da ba ta dace ba, ko muzguna wa 'yan adawar siyasa? Sai ya ce ba zai yi ba, ''in ban da a ranar farko''. "A...
Yadda manoma ke kwana a gonaki domin gadin amfanin gonarsu a jihar Yobe

Yadda manoma ke kwana a gonaki domin gadin amfanin gonarsu a jihar Yobe

Duk Labarai
A Najeriya, ana ci gaba da nuna damuwa kan yadda tsananin sata ke tilasta manoma fara kwana a gonakinsu domin gadi saboda yadda ɓarayi suka addabe su da satar amfanin gonakinsu. A jihar Yobe da ke yankin arewa maso gabas - inda aka samu rahoton ƙamarin lamarin - manoma da dama sun fara tarewa a gonakinsu ne musamman a cikin dare, wasu kuma aka tilasta musu su girbe amfanin ko da kuwa ba su isa girba ba saboda gudun kada su yi asara baki ɗaya. Daga cikin ƙananan hukumomin da matsalar ta fi ƙamari akwai Gujiba, da Damaturu, da Gashuwa, da sauransu. Lamarin ya kai ga wasu manoman na ɗaukar hayar mutane domin taya su gadi a gonakinsu, inda suke kwana ido biyu. Wannan matsala ba za ta rasa nasaba da yanayin da ake ciki a Najeriya ba na tsadar rayuwa, da hauhawar farashin kayan masar...
Nan da shekarar 2027 zamu gyara wutar lantarki ta yanda za’a rika samunta tsawon awanni 20 kullun>>Gwamnatin Tarayya

Nan da shekarar 2027 zamu gyara wutar lantarki ta yanda za’a rika samunta tsawon awanni 20 kullun>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya tace nan da shekarar 2027 zata samar da wutar Lantarki ta awanni 20 kullun. Saidai tace sharadin hakan shine sai ta samu maau zuba jari a bangaren Fetur da iskar gas wanda a yanzu babu su sosai. Me baiwa shugaban kasa shawara akan makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana haka a wata ziyara da ta kai kasar Africa ta kudu. Tace za'a mayar da hankali ne wajan samarwa Birane da masana'antu karfin wutar lantarkin.

Maganin sanyi kowane iri

Magunguna
MAGANIN SANYI KOWANE IRI INSHA ALLAH Ga masu fama da ciwon sanyi kowanne iri ne insha Allah in suka bi wannan hanya zasu samu sauki,ko masu yawan tari da nura da ciwon gobobi da rikewar baya da kwankwaso da kaikayin jiki dadai sauran illolin da sanyi ke haifar wa. ABIN DA ZAA NEMA. Garin Tafarnuwa 2.Nono mekyau madara ta ruwa mekyau) YADDA ZAA HADA Zaa samu garin Tafarnuwa mai kyau sai a debi chakali daya a zuba a nono rabin kofi a juya asha da safe haka ma zaai da yamma,wato sau biyu a rana. Insha Allah indai an samu garin mai kyau akai kamar na sati 2 zaaga Nasara sosai cikin YARDAR ALLAH Allah yabada lafiya da zaman lafiya
Da Duminsa: Wutar Lantarkin Najeriya ta sake lalacewa a Yau Alhamis

Da Duminsa: Wutar Lantarkin Najeriya ta sake lalacewa a Yau Alhamis

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wutar Lantarkin Najeriya ta sake lalacewa a Yau Alhamis, 7/11/2024. Hutudole ya samu rahoton cewa wutar lantarkin ta lalace ne da misalin karfe 11:20am na yau Alhamis. Hukumar Nigeria National Grid ce ta tabbatar da hakan Wannan ne karo na biyu da wutar ta lalace a cikin satin da muke sannan karo na 12 a cikin wannan shekarar da muke ciki.