Sunday, April 19
Shadow

Duk Labarai

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Wasu ‘yan Najeriya 2 da aka kama a kasar Faransa sunje Chirani ba bisa ka’ida ba suna ta rokon dan Allah kar a dawo dasu Najeriya

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Wasu ‘yan Najeriya 2 da aka kama a kasar Faransa sunje Chirani ba bisa ka’ida ba suna ta rokon dan Allah kar a dawo dasu Najeriya

Duk Labarai
Wannan Bidiyon wasu 'yan nah ne da aka kama a kasar Faransa sun je Chirani ba bisa ka'ida ba. An gansu suna durkusa kasa suna rokon dan Allah kada a dawo dasu gida. https://twitter.com/i/status/2039689578815136181 https://www.youtube.com/watch?v=35Be5p0_360?si=wpgjZ6Cdn6SjxX3T
Tinubu ya gayamin yayi makarantar Allo, kuma ni na hanashi kaiwa Qasar Nijar Khary, Sannan ni nasashi ya kyale Dangote yayi matatarsa>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Tinubu ya gayamin yayi makarantar Allo, kuma ni na hanashi kaiwa Qasar Nijar Khary, Sannan ni nasashi ya kyale Dangote yayi matatarsa>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Sani Yahya Jingir ya bayyana amfanin gwamnatin Muslim Muslim. Yace shine ya je ya hana Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kaiwa Qasar Jihar Khary. Ya bayyana cewa kuma shine ya baiwa Shugaba Tinubu baki ya kyale Dangote ya ci gaba da matatar mansa. Yace kuma Tinubu ya gaya masa cewa yayi makarantar Allo. https://www.tiktok.com/@saleemyusufmuhammadsambo/video/7624969830562663687?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7624969830562663687&source=h5_m&timestamp=1775387910&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_camp...
Sun bashi gida, da Mota da jami’an tsaro sosai, yana tafiya kamar wani Gwamna>>Atiku Abubakar yayi magana akan Nafiu Bala Gombe da ya kaisu Kotu yace shine Shugaban ADC na gaskiya

Sun bashi gida, da Mota da jami’an tsaro sosai, yana tafiya kamar wani Gwamna>>Atiku Abubakar yayi magana akan Nafiu Bala Gombe da ya kaisu Kotu yace shine Shugaban ADC na gaskiya

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, Masu daukar nauyin Nafiu Bala Gombe da ya kaisu kotu yace shine shugaban APC na gaskiya sun bashi gida sun bashi mota sannan sun bashi jami'an tsaro sosai yana tafiya kamar wani Gwamna. Atiku ya bayyana hakane a hirar da DWHausa suka yi dashi. Duk da dai bai kira sunan Nafiu Bala Gombe ba amma da yawa sun fassara cewa Atiku dashi yake. Atiku yace anawa ADC wannan zagon kasar ne saboda karbuwar data samu a hannun al'ummar Najeriya. Saidai yace hakan bai hana mutane na ta kara yin tururuwa zuwa cikin jam'iyyar ba.

Kalli Bidiyon: Yanda aka rika rabawa mutane 500, 1000, da 2000 dan au je wajan Tarbar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ga wasu na rabawa mutane kudade, 500, 1000 da kuma 2000 wai dan su je wajan tarbar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf. A jiya ne dai Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma Kano bayan shafe kwanaki 10 a wajan babban taron jam'iyyar APC na kasa. https://twitter.com/i/status/2040423682196062311
Kalli Bidiyon: Kwankwaso mu gaya maka ko mu bari Duniya ta gaya maka? Cin amanar da Gawuna zai maka ba’a taba maka irinta ba>>Inji Hadimar Gwamnan Kano, Maryam Jan Kunne

Kalli Bidiyon: Kwankwaso mu gaya maka ko mu bari Duniya ta gaya maka? Cin amanar da Gawuna zai maka ba’a taba maka irinta ba>>Inji Hadimar Gwamnan Kano, Maryam Jan Kunne

Duk Labarai
Hadimar gwamnan jihar Kano, Kuma tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Jan Kunne ta bayyana cewa shin su gayawa Kwankwaso gaskiya ko su bari Duniya ta gaya masa? Tace irin cin amanar da Gawuna zaiwa Kwankwaso ba'a taba masa irin ta ba. Tace shima sai ya hanashi shiga Kano kamar yadda Ganduje ya masa. https://www.tiktok.com/@amb_nura_nitel/video/7625168863738481941?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7625168863738481941&source=h5_m&timestamp=1775379796&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android...
Da Duminsa: An bayyana yawan kudaden da ake zargin an baiwa Nafiu Bala dan ya kawo tarnaki a jam’iyyar ADC

Da Duminsa: An bayyana yawan kudaden da ake zargin an baiwa Nafiu Bala dan ya kawo tarnaki a jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Wasu Rahotanni sun yi zargin cewa kudi aka baiwa Nafiu Bala Gombe da yake ikirarin shine shugaban jam'iyyar ADC har ma ya kai su Atiku Kotu. Rahotan yace an baiwa Nafiu Naira Biliyan 2 ne ya kawo wannan rikici a cikin jam'iyyar ADC. Hakanan rahoton yace Nafiu yanzu ya fara buya baya shiga cikin mutane sosai. A ranar 7 ga watan Afrilu ne dai ake sa ran sake komawa kotu dan ci gaba da shari'ar ta ADC inda ake tsammanin su Atiku zasu nemi kotun ta yi watsi da karar. https://twitter.com/i/status/2040658724059009259
Ji Abinda Arteta yace bayan da Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton

Ji Abinda Arteta yace bayan da Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton

Duk Labarai
Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Southampton da ci 2-1 wanda ya fitar da ita daga gasar cin kofin FA Cup. A martaninsa bayan wasan, Kocin Arsenal Arteta ya bayyana cewa, ba zai soki yaransa ba. Yace sun shafe watanni 9 suna kokari ma kungiyar dan sun yi rashin nasara a wannan wasan ba zai sokesu ba, yace amma shine ya dauki alhakin wannan rashin nasara.
Da Duminsa: Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da Seyi Makinde na Oyo da wasu ‘yan majalisar tarayya sun fasa komawa jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Gwamna Bala Mohammed na Bauchi da Seyi Makinde na Oyo da wasu ‘yan majalisar tarayya sun fasa komawa jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Muhammad da Takwaransa na jihar Oyo, Seyi Makinde sun fasa shirinsu na komawa jam'iyyar ADC. Rahoton jaridar Punchng ya bayyana cewa, Gwamnonin sun dakatar da aniyarsu ne biyo bayan cite sunayen shuwagabannin ADC da INEC ta yi daga kundin tattara bayananta. Hakanan Wasu 'yan majalisar tarayya dake shirin komawa jam'iyyar ta ADC suna sun fasa saboda wannan rikicin da ya mamaye jam'iyyar ta ADC. INEC ta sanar da cewa, zata jira sai bayan hukuncin kotu kamin su yanke shawara kan shuwagabannin jam'iyyar ADC.
Kalli Bidiyon: Na yi Ministan wutar Lantarkin na tara kudi iya kudi ta yanda ko da ban sake neman wani mukamin siyasa ba bazan yi talauci ba>>Inji Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu

Kalli Bidiyon: Na yi Ministan wutar Lantarkin na tara kudi iya kudi ta yanda ko da ban sake neman wani mukamin siyasa ba bazan yi talauci ba>>Inji Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu

Duk Labarai
A wani Bidiyo dake ta yawo a kafafen sada zumunta an ga Ministan wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu yana bayyana cewa ya tara kudi. Ta yanda ko da bai sake neman wani mukamin gwamnati ba ba zai yi talauci ba. https://twitter.com/i/status/2040503475293851651