Saturday, April 25
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Matasa sun fito Zanga-zanga a jihar Edo inda suka ce kada wanda ya sake ya kawo musu shinkafar da shugaba Tinubu ke rabawa tallafi, basaso dan su ba mayunwata bane

Kalli Bidiyon: Matasa sun fito Zanga-zanga a jihar Edo inda suka ce kada wanda ya sake ya kawo musu shinkafar da shugaba Tinubu ke rabawa tallafi, basaso dan su ba mayunwata bane

Duk Labarai
Matasa a jihar Edo sun fito zanga-zanga inda suka ce basa son tallafin shinkafar da Gwamnatin tarayya ke rabawa. Sun bayyana cewa su ba shinkafa bace matsalar su, ta yaya, Duk wata matsala da ake da ita, shinkafa kawai za'a kawo? Matasan sun ce abin ya isa haka: https://twitter.com/i/status/2039286568280523130
Da Duminsa: An gama zaman Kotu ba tare da kotun ta bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba, Sannan ICPC sun Mikashi hannun DSS

Da Duminsa: An gama zaman Kotu ba tare da kotun ta bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba, Sannan ICPC sun Mikashi hannun DSS

Duk Labarai
Rahotanni daga babbar kotun tarayya dame Kaduna inda ake shari'ar tsohon Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sun bayyana cewa. Lauyoyin Tsohon gwamnan sun nemi a bayar da belinsa sannan suma Lauyoyin Gwamnati sun bayar da nasu bayanan. Bayan kammala sauraren kowanne bangare, Kotun tace ta saka ranar 14 ga watan Afrilu dan yanke hukunci kan shari'ar. Saidai wannan rana ta yi daidai da ranar babban taron jam'iyyar ADC na kasa, inda wasu ke zargin da gangan aka yi hakan. https://twitter.com/i/status/2039320096514925046
Wata Sabuwa: An kama Direban Matar sarkin Kano da zargin satar Gwal na Naira Miliyan sittin

Wata Sabuwa: An kama Direban Matar sarkin Kano da zargin satar Gwal na Naira Miliyan sittin

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, an gurfanar da direban matar me martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II da wasu mutane 2 a gaban kotun Magistrate dake Nomansland a Kano. Ana zarginsu ne da satar Gwal na Naira Miliyan 60 da kuma karbar kayan sata. Wadanda ake zargin sune Sulaiman Yakubu Kulkude, Idris Musa, da Abdullahi Usaini. Hakanan ana zarginsu da satar kudi da kuma wayar hannu. Yayin zaman kotun, Sulaiman ya amsa duka laifukan da akw zarginsu da aikatawa saidai sauran biyun da ake zargi sun musanta zargin da ake musu. Lauyan wadanda ake zargin, Barrister A.A. Abdullahi ya bukaci a bashi belin wadanda ake zargin inda mai shari'a, Magistrate Halilu Abdurahman ya bayar da belin da sharuda masu tsanani. Yace dole duk wanda zai karbi belinsu ya zamana ma'aikacin Gwamnati dake ...
Fadar shugaban kasa, ta sai Dutsen Guga guda biyu akan Naira Miliyan 10

Fadar shugaban kasa, ta sai Dutsen Guga guda biyu akan Naira Miliyan 10

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun bayyana cewa, Fadar ta sayi Dutsen guga guda biyu akan Naira Miliyan 10. Watau kowanne dutsen guga an sayeshi akan Naira Miliyan 5 kenan. An saiwa ofishin mataimakin shugaban kasa, wannan Dutsen gugar ne, kamar yanda kafar dake saka ido akan yanda ake kashe kudin Gwamnati, Govspend ta ruwaito. Lamarin dai ya baiwa mutane mamaki.
Da Duminsa:Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a kotu a yau sanye da tutar jam’iyyar ADC

Da Duminsa:Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a kotu a yau sanye da tutar jam’iyyar ADC

Duk Labarai
A yau, Laraba, Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana a gaban babbar kotun tarayya dake Kaduna inda kotun zata saurari bukatarsa ta neman beli. Wani abu da ya dauki hankula shine ganin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da hatimin jam'iyyar ADC a jikin rigarsa. An baza jami'an tsaro a farfajiyar Kotun inda aka hana zirga-zirga a wajan. Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na fuskantar tuhume-tuhumen aikata ba daidai ba a ofishinsa da kuma almundahanar kudade.
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na ta shan yabo saboda irin kulawar da ya baiwa Mahaifiyarsa lokacin tana raye, ko da yana Gwamna yana bata lokaci sosai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na ta shan yabo saboda irin kulawar da ya baiwa Mahaifiyarsa lokacin tana raye, ko da yana Gwamna yana bata lokaci sosai

Duk Labarai
Jama'a da yawa a kafafen sada zumunta sai yabon Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai suke yi saboda irin kulawar da ya baiwa mahaifiyarsa lokacin tana raye. Ko da yana Gwamna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya rika baiwa Mahaifiyarsa Lokaci sosai yana bata kulawa. Wani Bidiyo da aka gani na mahaifiyar Nasiru tana yaba masa tana masa kirari ya karade kafafen sada zumunta sosai. https://twitter.com/i/status/2039049027904266607
Rahotanni naa cewa akwai yiyuwar Rarara zai bar jam’iyyar APC zuwa ADC

Rahotanni naa cewa akwai yiyuwar Rarara zai bar jam’iyyar APC zuwa ADC

Duk Labarai
Wasu rahotanni dake yawo a kafafen sada zumunta sun bayyana cewa Tauraron mawakin siyasa Dauda Kahutu Rarara na shirin barin jam'iyyar APC zuwa ADC. Rahoton yace abinda ya batawa Rarara rai har yake shirin barin jam'iyyar ta ADC shine rashin tafiyar da ba'a yi dashi ba zuwa kasar Ingila da shugaba Tinubu ya kai ziyara. An dai hangi mawakiyar kudu, Tiwa Savage a cikin tawagar shugaba Tinubu a ziyarar da ya kai Ingilar inda aka rika cece-kuce cewa ba a dauki mawakin Arewa ko guda a cikin tafiyar ba. Zuwa yanzu dai babu abinda Rarara yace akan lamarin. https://twitter.com/i/status/2039102682473124306
ICPC ta sake kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan zaman kotun yau

ICPC ta sake kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan zaman kotun yau

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar ICPC ta sake kama tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a yau bayan zaman kotun da aka yi. Malam Nasiru Ahmad El-Rufai dai ya nemi beli inda kotu ta saka ranar Laraba, 1 ga watan Afrilu dan yanke hukunci. A baya dai ICPC sun ce sun saki malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne saboda tausayi bayan rasuwar mahaifiyarsa inda ya samu halartar jana'izar da aka mata. https://twitter.com/i/status/2038967971477962970
Da Duminsa:  Rahotanni na cewa, wasu matasa sun yiwa Musa Mai Sana’a na jaki

Da Duminsa: Rahotanni na cewa, wasu matasa sun yiwa Musa Mai Sana’a na jaki

Duk Labarai
Rahotanni na ta yawo a kafafen sada zumunta inda ake yada cewa wasu matasa sun tare Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a inda suka masa na jaki. Shafin @kafinhausa dake X ya wallafa cewa, lamarin ya farune a Sharada dake Kano. Mai Sana'a dai bai tabbatar da hakan da kansa ba, sannan babu wata kafa data kawo labarin, saidai labarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta inda mutane ke ta bayyana ra'ayoyinsu akai. https://twitter.com/i/status/2038737606788149299